Samfuri:Kanun labarai
Appearance
Shafukan da ake bukatar a ƙara inganta su
![](http://chped.net/https/upload.wikimedia.org/wikipedia/commons/thumb/5/50/SE2024Apr08T.gif/100px-SE2024Apr08T.gif)
- Ƙungiyar gwamnonin arewa maso yammacin Najeriya ta kafa wani kwamiti da zai rika tuntubar juna da aiwatar da abubuwan da aka cimma bayan, kammala taron inganta zaman lafiya da tsaro a yankin da aka gudanar a Katsina.
- Shugaban kasar Nijar Abdourahamane Tchani ya gana da tsoffin shugabannin kasar Bénin Nicephore Soglo da Boni Yayi a Yamai
- Shugaban tarayyar Najeriya Bola Tinubu ya ce zai tuntubi gwamnonin jihohi kafin yanke shawarar karshe game da sabon tsarin albashi
- A jamhuriyar kasar Mali, faraministan kasar Choguel Kokalla Maiga, ya gana tare da Abdou Adamou jakadan kasar Nijar dake Mali a ranar jiya 24 ga watan Junin shekarar 2024 a fadar faraministan kasar Mali dake birnin Bamako.
- Julian Assange da ya kirkiro shafin kwarmata bayanai na WikiLeaks, ya amsa aikata laifi guda na keta dokar cin amanar kasa a wata babbar kotun tarayya dake Saipan, babban birnin Arewacin Tsibirin Mariana, a matsayin wani bangare na yarjejeniyar da ya cimma da ma’aikatar shari’a ta Amurka, domin kaucewa kara zaman kaso, tare da kawo karshen shari’ar da aka dauki shekaru ana yi.