Jump to content

Safa da Marwa

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Safa da Marwa
religious behaviour (en) Fassara
Bayanai
Bangare na Aikin Hajji da Sa'yee (en) Fassara
Ƙasa Saudi Arebiya
Wuri
Map
 21°25′25″N 39°49′38″E / 21.423611111111°N 39.827222222222°E / 21.423611111111; 39.827222222222
safa da marwa

الصّفا, Aṣ-Ṣafā) da (المروا, Al-marwa) wasu ƙananan tsaunuka ne da suke a Babban Masallacin Makkah a Saudi Arabia da ake masa laƙabi da suna Masjid Al-Haram. Musulmai na kaiwa da dawowa sau bakwai a tsakanin su lokacin aikin Hajji da Umrah. Sun kasance a tsakiyar birnin Makkah, kewaye da gidajen mazauna birnin, tare da Dar al-Arqam. Yin gudanarwan aikin yasamo asali ne tun daga lokacin jahiliyyan larabawa kafin zuwan musulunci, waɗanda suka yarda da cewa As-Safa da Al-Marwah wasu masoya ne guda biyu waɗanda ubangijinnin suka narkar dasu saboda aikawa zina kamar yadda aka rawaito su a a hadith da dama. Al'adar zagaye As-Safa da al-Marwah ansanya shi acikin ayyukan aikin hajji tareda wasu ayyukan da suka kasance ana aikata su kafin zuwan musulunci.[1]

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. Al-Bukhari, Muhammad (846). Sahih of al-Bukhari, Vol. 2. p. 195.


Wannan Muƙalar guntuwa ce: tana buƙatar a inganta ta, kuna iya gyara ta.