Hassana Abdullahi
Hassana Abdullahi Jaruma ce a masana'antar fim ta Hausa wato kannywood ta Dan jima a masana'antar tayi fina finai da dama a masana'antar tare da yar uwarta Hussaina.[1]
Tarihin[gyara sashe | gyara masomin]
Cikakken sunan ta shine Hassana Musa Abdullahi , jaruma ce a masana'antar fim ta Hausa wato kannywood. An haifeta tare da yar uwarta hussaina a ranar 20 ga watan fabrairu shekarar 1995 a unguwa uku Karamar hukumar Tarauni a cikin jihar [2]kano. Sun girma ita da yar uwarta a cikin garin Kano,haka zalika su yaren Hausa ne da kuma Fulani .
Karatu[gyara sashe | gyara masomin]
Jarumar tayi karatun firamare tare da yar uwarta hussaina a makarantar dake unguwa uku special primary school, sunyi karatun sakandiri a government girls secondary school Johanna a garin kano. Bayan ta gama hassana ta shiga kwalejin Aminu Kano inda tayi difloma ta Karanci Islamic and legal studies, inda ta gama a shekarar 2014.[3]
Masana'antar Fim[gyara sashe | gyara masomin]
Hassana ta Sami shiga masana'antar ita da yar uwarta Hussaina ta hanyar abokin Hussaina na makaranta Wanda darakta ne a masana'antar. Farko Yana Kiran su suga yanda ake yin fim din daga Nan suke Sha,awan fim din. Sun shiga masana'antar fim a shekarar 2013.[4]
- Fina Finan Ta
- Juyin Mulki
- fitsarin fako
- Mairon kauye
- Ibro Dan karota
- duka biyu
- Sabon Dan tijara
Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]
- ↑ https://www.blueprint.ng/i-wont-wait-for-my-twins-if-i-get-suitor-hassana-musa-abdullahi/
- ↑ https://www.pressreader.com/nigeria/daily-trust-saturday/20160123/281702613727649
- ↑ https://hausa.legit.ng/1145901-kannywood-yadda-wasu-tagwaye-ke-sharar-fage-a-shirin-fim.html
- ↑ "Kwafin ajiya". Archived from the original on 2023-07-30. Retrieved 2023-07-30.